Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, sheikh mahmud Shuhat ya gabatar da karatun kur'ani mai tsarki aya ta 37 a cikin surat Fussilat, wadda take magana a kan ayoyi da suke nuni da samuwar ubangiji, daga cikinsu kuwa rana da wata da halittar sammai da kassai da sauransu.
Ya yi wannan karatu ne a cikin makon da ya gabata a cikin Dihqaliyya na kasar masar tare da halartar jama'a.
Cibiyar musulunci ta Imam Ali (AS) da ke birnin hamburg na kasar Jamus ce take daukar nauyin saka wadannan karatuka.