Tashar Almayadeen ta bayar da rahoton cewa, majiyoyin gwamnatin yahudawan Isra’ia sun sanar da cewa, an kai wa katafaren jirgin ruwan hari ne a lokacin day a yake kan hanyarsa ta zuwa kasar Hadaddiyar Daular Larabawa daga gabar ruwan Jiddah a kasar Saudiyya.
Jirgin yahudawan dai yana dakon danyen man fetur ne, wanda kuma mallaki na kamfanin Isra’ila, inda kuma har yanzu babu wata kungiya ko wani bangare da ya sanar da alhakin kai harin.
Sai tuni jami’an gwamnatin yahudawan Isra’ila suka sanar da cewa, suna gudanar da bincike domin tabbatar da cewa ko Iran tana da hannu a cikin lamarin.