Shafin Standard Media ya bayar da rahoton cewa, saki mutanen da suke aiki a wata cibiyar musulunci a birnin Nairobi na kasar Kenya bayan sace su na tsawon kwanaki goma sha biyu.
Bayanin ya ce daga cikin mutanen uku akwai daraktan cibiyar, da kuma wasu maa’ikata biyu, wadanda aka sace su tun ranar 15 ga watan Agusta, ba tare da sanin dalilin hakan ba.
Amma a ranar Litinin da ta gabata an kawo su a kusa da birnin Nairobi aka sake su, amma idanunsu a rufe, sai dai jami’an ‘yan sanda sun sanar da cewa suna gudanar da bincike kan lamarin, domin gano wadanda suke da hannu a cikin wannan lamari.