IQNA

Macron: Matsayar Da Trump Dangane Da Birnin Quds A Babban Kure Ne

22:20 - March 08, 2018
Lambar Labari: 3482462
Bangaren kasa da kasa, shugaban kasar Faransa Emanuel Macron ya bayyana cewa, matsayar da shugaban Amurka Donald Trump ya dauka dangane da birnin Quds babban kure ne.

 

Tashar talabijin ta Alwatan ta bayar da rahoton cewa, a lokacin da yake gabatar da wani jawabi a gaban wani taro da yahudawa suka shirya a Faransa, Macron ya bayyana cewa amincewa da Quds a matsayin babban birnin Isra’ila baa b ne da zai taimaka wajen warware matsalar da ke tsakanin Isra’ila da Palastinawa ba.

Macron ya ce irin wannan mataki babu abin da zai kara illa dagula lamurra, maimakon hakan a cewarsa, kamata ya yi a karfafa batun tattaunawa tsakanin bangarorin biyu domin su warware matsalarsu ta hanyar fahimtar juna.

Tun bayan da Trump ya ayyana birnin Quds a matsayin babban birnin Isra’ila, yake ci gaba da shan suka daga ciki da wajen Amurka, har daga manyan kawayen Amurka na yammacin turai.

3698063

 

 

 

 

 

captcha