Tashar Alkafil ta bayar da rahoton cewa, ana ci gaba da zaman karbar gaisuwar Ayatollah Sayyid Hakim Babban malami da Allah ya yi masa rasuwa a Iraki kwanaki tara da suka gabata.
Bayan ga zaman majalisin karbar gaisuwa a Najaf, ana wani majalisin a Karbala tsakanin hubbaren Imam Hussain (AS) da Abul Fadl (AS).
Ayatollah Sayyid Muhammad Said Hakim yana daga cikin manyan malaman mazhabar Ahlul bait (AS) wanda ya rasu a ranar Juma'ar wancan makon da ya gabata, sakamakon tsayawar zuciya.