IQNA

Kira Zuwa Ga Karfafa Hadin Kai Tsakanin Musulmin Zimbabwe

23:56 - June 25, 2019
Lambar Labari: 3483771
Bangaren kasa da kasa, mai bayar da fatawa na kasar Zimbabwe ya jaddada wajabcin kafafa hadin kai tsakanin al'ummar musulmi an kasar Zimbabawe.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, musulmin kasar Zimbabwe sun gudanar da wani babban taro a birnin Kampala fadar mulkin kasar.

Isma'ila Menk babban mai bayar da fatawa na kasar ta Zimbabwe ya gabatar da jawabia  wurin wannan taron, inda ya jaddada wajabcin kafafa hadin kai tsakanin al'ummar musulmi an kasar Zimbabawe.

Ya ce a halin yanzu bababn abin da musulmi suke bukata shi ne hadin kai, su ajiye kyamar junasu saboda banbancin fahimta kan wasu abubuwa wadanda ba su ne asali da tushen addini ba.

Menk ya ce addinin musulunci addinin sulhu da fahimtar jun ne na nuna kyama da adawa da kin juna ba,a  kan haka dole ne musulmi su hada kai a tsakaninsu domin yin aki tare.

Mufti Menk ya ce yana kiran matasan musulmi na Zimbabwe da su zama masu yin hidima ga kowa musulmi da wanda ba musulmi a, domin wannan ita e koyarwar musulunci. 

3821879

 

captcha