Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa,a lokacin da Sheikh Abdulmumin Dalahu daya daga cikin manyan malaman kasar Ghana yake ganawa da karamin jakadan Iran a Ghana Muhammad Hassan Ipikchi, ya bayyana takunkumin Amurka kan Iran da cewa bai zai taba rusa Iran ba.
Shehin malamin ya ce tun bayan juyin juya halin muslunci Iran ta tabbatar wa duniya cewa takunkumi baya kara mata komai sai ci gaba da kuma dogaro da kanta, wanda a cewarsa Iran ta kai matsayinta na yanzu sakamakon takunkuman da aka yi ta kakaba mata ne.
Daga karshe ya mika sakon ta’aziyya ga al’mmar Iran baki daya dangane da harin ta’addancin da aka kai a birnin Ahwaz a kwanakin baya, tare da bayyana hakan da cewa aiki ne na dabbanci.